Banner
Want to Advertise Here
Labarai

Gwamnatin Kebbi na binciken cinikin taki

Wednesday, 19 October 2011 Written by

Gwamna Sa'idu Dakingari na jihar Kebbi ya  kafa kwamitin da zai bincike zargin almundahana a cinikin takin da aka yi a jihar daga shekarar 2001 zuwa 2011.

Babban sakatare a ofishin gwamnan, Alhaji Shuaibu Diri ya ce an dorawa kwamitin alhakin gano adadin takin da gwamnatin jihar ta saya da kuma abinda ta samu a cinikin.

Haka kuma kwamitin zai duba adadin takin da masu sayarwar suka karkatar sannan ya bada shawara kan hukuncin da ya dace gwamnatin ta yi musu.

Babban sakataren yace gwamnatin ta baiwa kwamitin wa'adin watanni biyu ne ya kammala aikinsa.

Najeriya za ta kara filayen jiragen sama

Wednesday, 19 October 2011 Written by

Ministar sufurin jiragen sama, Mrs. Stella Oduah ta bayyana shirin gwamnatin tarayya na kara adadin filayen saukar jirage a Najeriya.

Mrs. Oduah ta baiyana haka ne yayin da ta baiyana gaban kwamitin sufurin jiragen sama na majalisar dattawa ta kasa.

Ministar ta ce tsofaffin ma'aikata da tsofaffin kayan aiki su ne su ka addabi filayen tashin jiragen sama a fadin kasar.

Ta kuma ce burinta shi ne sufurin jiragen sama ya rinka samar da kaso 30 cikin 100 na arzikin da Najeriya ke da shi.

Umar Abdulmutallab zai koma kotu

Tuesday, 04 October 2011 Written by

A ranar Talata ne ake sa ran ci gaba da shari'ar da ake yiwa dan Najeriya Umar Farouk Abdulmutallab kan zargin yunkurin tada bam a wani jirgin saman Amurka a shekarar 2009.

A ranar Kirsimetin shekara ta 2009 ne aka kama Abdulmutallab a kan hanyarsa ta zuwa Detroit a Amurka, inda kuma aka zarge shi da yunkurin tayar da bam a jirgin.

An kama mutane bakwai akan harin Zamfara

Tuesday, 04 October 2011 Written by

'Yan sanda a Najeriya sunce sun cafke mutane bakwai da ake zargi da hannu a harin da aka kai a kauyen Lingyado dake jihar Zamfara.

Shugaba Karzai na Afghanistan ya sheda ma wani taron malaman addini cewa hanya daya tak ta samun zaman lafiya a Afghanistan ita ce ta tattaunawa da Pakisan, maimakon kungiyar Taleban.

Shugaba Karzai ya ce ba za a iya gano Majalisar Taliban ba ko kuma jagoranta Mullah Omar.

Obama ya yi farin ciki da kisan Al-Awlaki

Saturday, 01 October 2011 Written by

Shugaba Obama na Amurka ya tabbatar cewa an kashe daya daga cikin 'yan kungiyar Alqa'ida da ya fi tasiri, Ba'amerike, Anwar Al-Aulaqi.

A Yemen ne aka kashe shi.

An ce Al-Awlaqi ya taka muhimmiyar rawa wajen shiryawa da ba da umurni kisan Amerikawa.

Shugaba Obama ya bayyana farin cikinsa da kisan Al Awlaqin.

Ya ce, "Mutuwar Al-awlaqi babban gaci ne aka kai a babban yakin da ake yi da Alqa'ida da kuma sauran kungiyoyi kawayenta.

Sarkin Kano ya nemi gwamnatin tarayya ta inganta samar da wutar lantarki a sakonsa na hawan Nassarawa.

Ma’aikatan Pilato sun shiga yajin aiki

Monday, 05 September 2011 Written by

Ma’aikatan jihar Pilato sun fara yajin aiki bisa gazawar gwamnati wurin biyan mafi karancin albashin N18,000.